Arabic Ibn Kathir Tafseer
[بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ. رَبِّ يَسِّرْ بِفَضْلِكَ]
تَفْسِيرُ سُورَةِ الْقَصَصِ
[وَهِيَ مَكِّيَّةٌ]
قَالَ الْإِمَامُ أَحْمَدُ بْنُ حَنْبَلٍ، رَحِمَهُ اللَّهُ: حَدَّثَنَا يَحْيَى بْنُ آدَمَ، حَدَّثَنَا وَكِيع، عَنْ أَبِيهِ، عَنْ أَبِي إِسْحَاقَ، عَنْ مَعْدِ يكَرِبَ قَالَ: أَتَيْنَا عَبْدَ اللَّهِ فَسَأَلْنَاهُ أَنْ يَقْرَأَ عَلَيْنَا ﴿طسم﴾ الْمِائَتَيْنِ، فَقَالَ: مَا هِيَ مَعِي، وَلَكِنْ عَلَيْكُمْ مَن أَخَذَهَا مِنْ رَسُولِ اللَّهِ ﷺ: خَبَّاب بْنَ الأرَت. قَالَ: فَأَتَيْنَا خَبَّاب بْنَ الْأَرَتِّ، فَقَرَأَهَا عَلَيْنَا، رَضِيَ اللَّهُ عَنْهُ .
* * *
قَدْ تَقَدَّمَ الْكَلَامُ عَلَى الْحُرُوفِ الْمُقَطَّعَةِ.
* * *
وَقَوْلُهُ: ﴿تِلْكَ﴾ أَيْ: هَذِهِ ﴿آيَاتُ الْكِتَابِ الْمُبِينِ﴾ أَيْ: الْوَاضِحِ الْجَلِيِّ الْكَاشِفِ عَنْ حَقَائِقِ الْأُمُورِ، وَعِلْمِ مَا قَدْ كَانَ وَمَا هُوَ كَائِنٌ.
* * *
وَقَوْلُهُ: ﴿نَتْلُو عَلَيْكَ مِنْ نَبَإِ مُوسَى وَفِرْعَوْنَ بِالْحَقِّ لِقَوْمٍ يُؤْمِنُونَ﴾ كَمَا قَالَ تَعَالَى: ﴿نَحْنُ نَقُصُّ عَلَيْكَ أَحْسَنَ الْقَصَصِ﴾ [يُوسُفَ: ٣] أَيْ: نَذْكُرُ لَكَ الْأَمْرَ عَلَى مَا كَانَ عَلَيْهِ، كَأَنَّكَ تُشَاهِدُ وَكَأَنَّكَ حَاضِرٌ.
ثُمَّ قَالَ: ﴿إِنَّ فِرْعَوْنَ عَلا فِي الأرْضِ﴾ أَيْ: تَكَبَّرَ وَتَجَبَّرَ وَطَغَى. ﴿وَجَعَلَ أَهْلَهَا شِيَعًا﴾ أَيْ: أَصْنَافًا، قَدْ صَرَّفَ كُلَّ صِنْفٍ فِيمَا يُرِيدُ مِنْ أُمُورِ دَوْلَتِهِ.
* * *
وَقَوْلُهُ: ﴿يَسْتَضْعِفُ طَائِفَةً مِنْهُمْ﴾ يَعْنِي: بَنِي إِسْرَائِيلَ. وَكَانُوا فِي ذَلِكَ الْوَقْتِ خِيَارَ أَهْلِ زَمَانِهِمْ. هَذَا وَقَدْ سُلِّطَ عَلَيْهِمْ هَذَا الْمَلِكُ الْجَبَّارُ الْعَنِيدُ يَسْتَعْمِلُهُمْ فِي أَخَسِّ الْأَعْمَالِ، ويكُدُّهُم لَيْلًا وَنَهَارًا فِي أَشْغَالِهِ وَأَشْغَالِ رَعِيَّتِهِ، وَيَقْتُلُ مَعَ هَذَا أَبْنَاءَهُمْ، وَيَسْتَحْيِي نِسَاءَهُمْ، إِهَانَةً لَهُمْ وَاحْتِقَارًا، وَخَوْفًا مِنْ أَنْ يُوجَدَ مِنْهُمُ الْغُلَامُ الَّذِي كَانَ قَدْ تَخَوَّفَ هُوَ وَأَهْلُ مَمْلَكَتِهِ مِنْ أَنْ يُوجَدَ مِنْهُمْ غلام، يَكُونُ سَبَبُ هَلَاكِهِ وَذَهَابُ دَوْلَتِهِ عَلَى يَدَيْهِ. وَكَانَتِ الْقِبْطُ قَدْ تَلَقَّوْا هَذَا مِنْ بَنِي إِسْرَائِيلَ فِيمَا كَانُوا يَدْرُسُونَهُ مِنْ قَوْلِ إِبْرَاهِيمَ الْخَلِيلِ، حِينَ وَرَدَ الدِّيَارَ الْمِصْرِيَّةَ، وَجَرَى لَهُ مَعَ جَبَّارِهَا مَا جَرَى، حِينَ أَخَذَ سَارَّةَ لِيَتَّخِذَهَا جَارِيَةً، فَصَانَهَا اللَّهُ مِنْهُ، وَمَنَعَهُ مِنْهَا بِقُدْرَتِهِ وَسُلْطَانِهِ. فَبَشَّرَ إِبْرَاهِيمُ عَلَيْهِ السَّلَامُ وَلَدَهُ أَنَّهُ سَيُولَدُ مِنْ صُلْبِهِ وَذَرِّيَّتِهِ مَن يَكُونُ هَلَاكُ مَلِكِ مِصْرَ عَلَى يَدَيْهِ، فَكَانَتِ الْقِبْطُ تَتَحَدَّثُ بِهَذَا عِنْدَ فِرْعَوْنَ، فَاحْتَرَزَ فِرْعَوْنُ مِنْ ذَلِكَ، وَأَمَرَ بِقَتْلِ ذُكُورِ بَنِي إِسْرَائِيلَ، وَلَنْ يَنْفَعَ حَذَرٌ مِنْ قَدَرٍ؛ لِأَنَّ أَجَلَ اللَّهِ إِذَا جَاءَ لَا يُؤَخَّرُ، وَلِكُلِّ أَجَلٍ كِتَابٌ؛ وَلِهَذَا قَالَ: ﴿وَنُرِيدُ أَنْ نَمُنَّ عَلَى الَّذِينَ اسْتُضْعِفُوا فِي الأرْضِ وَنَجْعَلَهُمْ أَئِمَّةً وَنَجْعَلَهُمُ الْوَارِثِينَ. وَنُمَكِّنَ لَهُمْ فِي الأرْضِ وَنُرِيَ فِرْعَوْنَ وَهَامَانَ وَجُنُودَهُمَا مِنْهُمْ مَا كَانُوا يَحْذَرُونَ﴾ . وَقَدْ فَعَلَ تَعَالَى ذَلِكَ بِهِمْ، كَمَا قَالَ: ﴿وَأَوْرَثْنَا الْقَوْمَ الَّذِينَ كَانُوا يُسْتَضْعَفُونَ مَشَارِقَ الأرْضِ وَمَغَارِبَهَا الَّتِي بَارَكْنَا فِيهَا وَتَمَّتْ كَلِمَةُ رَبِّكَ الْحُسْنَى عَلَى بَنِي إِسْرَائِيلَ بِمَا صَبَرُوا وَدَمَّرْنَا مَا كَانَ يَصْنَعُ فِرْعَوْنُ وَقَوْمُهُ وَمَا كَانُوا يَعْرِشُونَ﴾ [الْأَعْرَافِ: ١٣٧] وَقَالَ: ﴿كَذَلِكَ وَأَوْرَثْنَاهَا بَنِي إِسْرَائِيلَ﴾ [الشُّعَرَاءِ: ٥٩] ، أَرَادَ فِرْعَوْنُ بِحَوْلِهِ وَقُوَّتِهِ أَنْ يَنْجُوَ مِنْ مُوسَى، فَمَا نَفَعَهُ ذَلِكَ مَعَ قَدَر الْمَلِكِ الْعَظِيمِ الَّذِي لَا يُخَالَفُ أَمْرُهُ الْقَدَرِيُّ، بَلْ نَفَذَ حُكْمُهُ وَجَرَى قَلَمُهُ فِي القِدَم بِأَنْ يَكُونَ إِهْلَاكُ فِرْعَوْنَ عَلَى يَدَيْهِ، بَلْ يَكُونُ هَذَا الْغُلَامُ الَّذِي احْتَرَزْتَ مِنْ وُجُودِهِ، وَقَتَلْتَ بِسَبَبِهِ أُلُوفًا مِنَ الْوِلْدَانِ إِنَّمَا مَنْشَؤُهُ وَمُرَبَّاهُ عَلَى فِرَاشِكَ، وَفِي دَارِكَ، وَغِذَاؤُهُ مِنْ طَعَامِكَ، وَأَنْتَ تُرَبِّيهِ وَتُدَلِّلُهُ وَتَتَفَدَّاهُ، وَحَتْفُكَ، وَهَلَاكُكَ وَهَلَاكُ جُنُودِكَ عَلَى يَدَيْهِ، لِتَعْلَمَ أَنَّ رَبَّ السَّمَوَاتِ الْعُلَا هُوَ الْقَادِرُ الْغَالِبُ الْعَظِيمُ، الْعَزِيزُ الْقَوِيُّ الشَّدِيدُ الْمِحَالِ، الَّذِي مَا شَاءَ كَانَ، وَمَا لَمْ يَشَأْ لَمْ يَكُنْ.
Arabic Baghawy Tafseer
الْمَلَائِكَةِ وُجُوهَهُمْ وَأَدْبَارَهُمْ، نَظِيرُهُ قَوْلُهُ عَزَّ وَجَلَّ: ["سَأُرِيكُمْ آيَاتِي فَلَا تَسْتَعْجِلُونِ" [الأنبياء: ٣٧] ، وَقَالَ مُجَاهِدٌ] سَيُرِيْكُمْ آيَاتِهِ فِي السَّمَاءِ وَالْأَرْضِ وَفِي أَنْفُسِكُمْ، كَمَا قَالَ: "سَنُرِيهِمْ آيَاتِنَا فِي الْآفَاقِ وَفِي أَنْفُسِهِمْ" [فصلت: ٥٣] ، ﴿فَتَعْرِفُونَهَا﴾ يَعْنِي: تَعْرِفُونَ الْآيَاتِ وَالدَّلَالَاتِ، ﴿وَمَا رَبُّكَ بِغَافِلٍ عَمَّا تَعْمَلُونَ﴾ وَعَدَهُمْ بِالْجَزَاءِ عَلَى أَعْمَالِهِمْ. سُورَةُ الْقَصَصِ
مَكِّيَّةٌ إِلَّا قَوْلَهُ عَزَّ وَجَلَّ: ﴿الَّذِينَ آتَيْنَاهُمُ الْكِتَابَ﴾ إِلَى قَوْلِهِ: ﴿لَا نَبْتَغِي الْجَاهِلِينَ﴾ وفيهالا آيَةٌ نَزَلَتْ بَيْنَ مَكَّةَ وَالْمَدِينَةِ، وَهِيَ قَوْلُهُ عَزَّ وَجَلَّ: ﴿إِنَّ الَّذِي فَرَضَ عَلَيْكَ الْقُرْآنَ لَرَادُّكَ إِلَى مَعَادٍ﴾ . ﷽
* * *
﴿طسم﴾
﴿تِلْكَ آيَاتُ الْكِتَابِ الْمُبِينِ﴾ ﴿نَتْلُوا عَلَيْكَ مِنْ نَبَإِ مُوسَى وَفِرْعَوْنَ بِالْحَقِّ﴾ بِالصِّدْقِ ﴿لِقَوْمٍ يُؤْمِنُونَ﴾ يُصَدِّقُونَ بِالْقُرْآنِ.
﴿إِنَّ فِرْعَوْنَ عَلَا﴾ اسْتَكْبَرَ وَتَجَبَّرَ وَتَعَظَّمَ ﴿فِي الْأَرْضِ﴾ أَرْضِ مِصْرَ ﴿وَجَعَلَ أَهْلَهَا شِيَعًا﴾ فِرَقًا وَأَصْنَافًا فِي الْخِدْمَةِ وَالتَّسْخِيرِ ﴿يَسْتَضْعِفُ طَائِفَةً مِنْهُمْ﴾ أَرَادَ بِالطَّائِفَةِ: بَنِي إِسْرَائِيلَ ثُمَّ فَسَّرَ الِاسْتِضْعَافَ فَقَالَ: ﴿يُذَبِّحُ أَبْنَاءَهُمْ وَيَسْتَحْيِي نِسَاءَهُمْ﴾ سَمَّى هَذَا اسْتِضْعَافًا لِأَنَّهُمْ عَجَزُوا وَضَعُفُوا عَنْ دَفْعِهِ عَنْ أَنْفُسِهِمْ ﴿إِنَّهُ كَانَ مِنَ الْمُفْسِدِينَ﴾KARATUN MALAMAN SUNNAH:
6.0. Ayyukan Ibada a Wajen 'Yan (Alƙur'ani Zalla):
6.2. Zakka a wajen 'yan Alƙur'ani Zalla (2)
Ci gaba….
Ra'ayin Alkhawaja Ahmaduddin da Mabiyansa:
Alkhawaja Ahmaduddin ya soki tsare-tsaren zakka da ke cikin littattafan hadisi da littattafan fiƙhu waɗanda al'ummar Musulmi suke aiki da su. Ya bayyana cewa, ko da a ce tsarin nisabin dukiyar da ake yi wa zakka da abin da ake fitarwa ya dace da zamanin da ya gabata, to a yanzu abubuwa sun canja, don haka bai dace a ci gaba da aiki da shi ba, domin nau'ukan dukiya a wancan zamani da wuce, watau zinar da azurfa da dabbobi da kayan amfanin gona, sun kansance akwai daidaito a cikin ƙimarsu. Amma a yanzu suna da bambanci sosai da tazara a tsakaninsu ta fuskar ƙima, don haka idan aka ci gaba da amfani da ma'auni irin na da, to masu son zuciya a cikin mawadata za su riƙa amfani da wannan bambanci wajen tauye haƙƙin talakawa yayin fitar da zakka.
Saboda da haka sai shi Alkhawaja yake ganin cewa, duk wani mai yin aiki a biya shi, to sai a haɗa masa da zakkarsa lokacin da aka zo biyansa ladan aikinsa, babu buƙatar a jira har tsawon shekara kafin a fitar da zakka.
To amma kuma abu ne sananne cewa, lokacin karɓar albashin ma'aikata ba ɗaya ne ba. Akwai wanda ake biyan sa kuɗin aikinsa a kullum; akwai kuma mai karɓa a duk mako; akwai wanda yake karɓar nasa a duk wata. Don haka a bisa ra'ayin Alkhawaja kullum sai mai dukiya ya fitar da zakkar dukiyarsa, ko dai ya bayar nan take ko kuma dai ya kimanta ta.
Sai dai abin lura dangane da ra'ayin Alkhawaja a kan zakka shi ne, bai bayyana gwagwadon abin da za a riƙa fitarwa na zakkar ba¸kawai dai shi yana magana ne a kan cewa, idan an tashi biyan ma'aikaci haƙƙin aikinsa, to a haɗa masa da zakkarsa a lokacin, kuma a ba shi abin da zai ishe shi.
Mabiyan Alkhawaja sun ci gaba da bin tafarkinsa wajen fitar da zakka. Almajirinsa Ibadullahi Akhtar ya bayyana cewa:
"Ya wajaba a raba zakka a bai wa kowa gwargwadon buƙatarsa ba tare da almubazzaranci ba, bisa la'akari da ma'aunin da ya dace da rayuwar mutum. Sannan dole ne ga Majalisar Shura ta Musulunci ta sanya ido wajen kula da dacewar wannan daidaito, duba da buƙatun rayuwa ta yau da gobe da lura da rashin tsayawar farashin kayayyaki a wuri ɗaya. Saboda haka dole ne ga Majalisar Shura ta fitar da dokoki da za su shafi zakka. Wannan ne ya sanya Alƙur'ani bai ƙayyade takamaiman lissafin nisabin zakka ba ko abin da za a fitar. Abin da kuma a yau ake aiki da shi na ƙayyade nisabi, Umar ne ya aiwatar da shi bayan ya nemi shawarar 'yan Majalisar Shura.. Don haka wannan ƙayyadewar tasa ijtihadinsa ne. Domin haka Majalisar Shura a yau tana da cikakken haƙƙi na su ƙayyade nisabin zakka da kuma gwargwadon abin da za a fitar, ta yadda zai dace da yanayin da ake ciki…".
Shi ma almajirin Alkhawaja, watau Sayyid Maƙbul ya bayyana cewa:
"Farilla huɗu ce a kan Musulmi. Guda biyu a cikin kowace rana, su ne, salla da zakka. Biyu kuma a cikin sherkara, su ne, azumi da hajji. Zakka daidai take da salla, ana aiwatar da ita ne a kullum ba tare da an gindaya mata sharaɗin cikar nisaba ba, ko zagayowar shekara ko kuma wani lokacin na musamman kafin a bayar da ita..".
Za mu ci gaba in sha Allah….
Alƙur'ani Zalla ko Bijire wa Manzon Allah (36)
6.0. Ayyukan Ibada a Wajen 'Yan (Alƙur'ani Zalla):
6.2. Zakka a wajen 'yan Alƙur'ani Zalla (3)
Ci gaba….
Ra'ayin Ghulam Ahmad Perwez:
Perwez yana da maganganu da yawa a kan zakka kamar yadda ya fahimce ta daga Alƙur'ani zalla.
A rubuce-rubucensa ya kira zakka da sunaye daban-daban, ya kira ta da zakka, a wani wuri kuma ya kira ta da 'rabon arzuki a Alƙur'ani', ya kuma kira ta da 'tsarin tattalin arzuki na Alƙur'ani', hakanan ya kira ta da 'harajin hukuma da alaƙarsa da zakka', ko 'tattalin arzuki' ko kuma 'ciyarwa don Allah', da sauransu.
Ya bayyana cewa:
"Ita zakka tana nufin samun haɓaka da ƙari. Alƙur'ani ya yi umarni da fitar da zakka inda ya ce: "Ku ba da zakka", wanda hakan yana nufin a ba wa mutum kayayyakin da za su haɓaka shi su ƙara masa samun hutu. Kuma ita wani farali ne a kan jama'ar muminai don taimaka wa mutane 'yan'uwansu. Su ba su abin da zai haɓaka su, ya kuma samar musu da ƙarin hutu. Zakka ita ce za ta haɓaka musu baiwar da Allah ya yi musu ta gangar jiki da ta ɗabi'u. Don haka Allah ya ce:
"( (Su ne) waɗanda, idan Muka kafa su a bayan ƙasa sai su tsai da salla su kuma ba da zakka ) [al-Hajji, aya ta 41].
"To a nan Alƙur'ani ya nuna zakka farali ne a kan hukumar Musulunci…".
Perwez ya ƙara da cewa:
"Abin tambaya a nan shi ne, ta ƙaƙa hukumar Musulunci za ta sauke nayin wannan farali na zakka daga kanta?
"Farko-farkon abin da zai taimaka wajen sauke wannan nauyi shi ne, a mayar wa da hukuma duk wasu hanyoyin samar da buƙatun rayuwa, ta yadda za ta iya biya wa mabuƙata buƙatunsu…"
Ya ci gaba da cewa:
"Sannan ba ya halatta wani ya ajiye abin da ya wuce buƙatarsa a gunsa, a'a dole ne ya mayar da dukiyar da fi ƙarfin buƙatarsa zuwa ga hukuma, don ta samu abin da za ta fitar da zakka zuwa ga mabuƙata. Don cimma wannan manufa ne ya sanya Alƙur'ani bai ayyana nisabi ko wani gwargwado na musamman ba. A'a, ya bar komai ya gudana a bisa la'akari da samun biyan buƙata da abin da yanayin rayuwa na yau da gobe ya hukunta".
"Don haka Alƙu'ani ya bayyana cewa, duk abin da ya wuce buƙatar mutum, to ya mayar da shi zuwa ga hukuma, domin ta samu abin fitar da zakka: (Allah) ya ce:
"(Kuma suna tambayar ka, me za su ciyar? Ka ce: “Abin da ya daɗu a kan buƙatunku.”) [Baƙara, aya ta 219]".
Mai karatu zai lura da cewa, fahimatar Perwez da mabiyansa game da zakka, ta yi kama da aƙidar 'yan gurguzu masu ganin cewa, ɗaiɗaikum mutane ba su da damar su mallaki wani abu nasu na kansu wanda ya wuce buƙatarsu. Don haka dukiya gaba ɗaya mallakin hukuma ce, sai abin da kawai mutum zai yi buƙatarsa da shi, wannan ne kaɗai mallakinsa.
Babu shakka wannan aƙida ta ci karo da koyarwar Musulunci baki ɗaya. Kai ta ma ci karo da ɗabi'ar halitta ita kanta. Kuma zakka a Musulunci ba ta nufin mutum ya ɗauki iya buƙatarsa a cikin dukiyarsa sauran ya mayar wa da hukuma. Wannan gurɓatacciyar fahimata ce, babu abin da zai goya mata baya a Alƙur'ani.
To mai karatu, wannan ita ce fahimtar ƙungiyoyi mabiya addinin 'Alƙur'ani zalla' a kan lamarin zakka, da irin yadda suka yi ta ɗirkaniya daban-daban wajen ganin sun samar da wani tsarin zakka saɓanin wanda Musulmi suke a kai, wanda suka gada daga koyarwar Manzon Allah (SAW) da sahabbai da limaman shiriya.
Za mu ci gaba in sha Allah…..
Alƙur'ani Zalla ko Bijire wa Manzon Allah (37)
6.0. Ayyukan Ibada a Wajen 'Yan (Alƙur'ani Zalla):
6.3. Azumi a Wajen 'Yan 'Alƙur'ani Zalla'
Azumi rukuni ne daga cikin rukunan Musulunci guda biyar. Allah ya farlanta wa Musulmi azumtar watan Ramadana a cikin kowace shekara, yayin da aka tabbatar da ganin watan Ramadan ko kuma watan Sha'aban ya cika kwanaki talatin.
Musulmi zai kame bakinsa daga ci da sha da kuma kusantar iyalinsa, tun daga hudowar alfijir har zuwa faɗuwar rana da niyyar bautar Allah.
Da dama daga cikin malaman mabiya addinin 'Alƙur'ani zalla' ba su saɓa da sauran Musulmi a wajen azumtar watan Ramadana ba, domin umarni da yin azumi a cikinsa ya zo ƙarara a cikin Alƙur'ani. Babu wanda ya bijire wa wannan umarni daga cikinsu sai Alkhawaja Ahmaduddin da Sayyid Muhammad Rafi'uddin.
Alkhawaja yana ganin cewa, Musulmi za su iya yin azumi a kowane wata suka ga dama, ba dole sai watan Ramadana ba. Idan sun ga dama su yi azuminsu kafin watan Ramadana, idan kuma sun ga dama su yi bayan watan Ramadan, watau gwargwadon yadda ya yi daidai da buƙatarsu a cewar Ahmaduddin. Ya kuma bayyana cewa, su ma magabata sun yi azuminsu ne a cikin Ramadana domin a cikinsa umarnin su yi azumi ya sauka gare su, ba don ya zama dole sai a cikinsa ba. [Duba, Tafsirinsa, Bayanun Lin-Nas, juz. 2, sh. 771-772].
Shi kuma Sayyid Muhammad Rafi'uddin yana ganin cewa, abin da yake wajibi a kan Musulmi shi ne, su yi azumin kwana talatin da lissafin kalandar bature, ba da ganin wata na Musulunci ba. Domin – a faɗarsa- lissafin watan bature shi ne baya canjawa. Amma lissafin Musulmi yana rage kwana goma a duk shekara. Sannan ya danganta lissafin ganin wata da cewa, lissafin kafirai ne, saboda Allah ya ce:
(Lalle jinkiri ba wani abu ba ne ban da ƙari cikin kafirci) [Tauba, aya ta37].
Watau yana nufin wannan ragin kwanaki goma da ake samu a duk shekara goma ta lissafin watanni, shi ne jinkirin da ake nufi a wannan ayar, alhalin ba haka abin yake ba ga duk wanda ya koma ya duba tafsirin ayar a wajen malaman tafisiri.
Saboda haka Rafi'uddin ya bayyana cewa, azumin Ramadana yana farawa ne daga ashirin da biyu ga watan Oktoba zuwa ashirin ga wata Nuwamba. Ya ƙara da cewa, yin azumi a waɗannan kwanaki ba zai cutar da lafiyar ɗan'adam ba. Kuma da haka ne faɗin Allah zai tabbata, watau inda yake cewa:
(Allah yana nufin sauƙi a gare ku. Kuma ba ya nufin tsanani a gare ku) [Al-Baƙara, aya ta 183].
A cikin mabiya addinin 'Alƙur'ani zalla' waɗanda suka fanɗare game da azumin Ramadana akwai: Maƙbul Ahmad da Alkhawaja Ibadullah Akhtar. Su waɗanna biyun, suna ganin azumin farilla wanda yake daidai da ruhin Alƙur'ani yana farawa ne daga ashirin da ɗaya ga watan Ramadana ya ƙare a safiyar ranar idi. Suka kafa hujja da faɗin Allah:
(Wasu kwanaki ne ƙididdigaggu) [Baƙara, aya ta 184].
Ya bayyana cewa, Kalmar "Ayyam" jam'i ne na "Yaum", kuma jam'i ne mai nuna ƙarancin adadi wanda yake farawa daga uku zuwa tara.
Don haka yana ganin kwanakin azumi su ne goman ƙarshe na watan Ramadana kaɗai, ba duka kwanakin watan ba.
Daga wannan ɗan bayani mai karatu zai fahimci cewa, waɗannan mutane masu ƙaryar bin 'Alƙur'ani zalla' ba a kan komai suke tafiya ba face ƙarerayi da son zuci. Babu abin da ya haɗa su da koyarwar Alƙur'ani. Dubi, yayin da Alƙur'ani a fili yake umartar muminai da su yi azuminsu na farilla a cikin watan Ramadana wanda Allah ya saukar da Alƙur'ani a cikinsa, inda ya ce:
(…Don haka duk wanda ya halarci wannan watan daga cikinku, to ya azumce shi..) [Al-Baƙara, aya ta 185].
![]() ![]() | |||||
| |||||
![]() | |||||
![]() | |||||
![]() | |||||
![]() | |||||
![]() | |||||
![]() | |||||
![]() | |||||
![]() | |||||
|
|